09/07/2024
Shi ne ya nemo ma jahar zamfara lasisin mallakar jami'a ta kashin kanta.
Shi ne ya samar da filin da aka soma gina jami'ar bayan ya biya diyyar masu filaye.
Shi ne ya soma assasa ginin jami'ar, duk wanda ya zo sai dai ya dora a bayan sa.
Shi ne ya samar ma ta da mazauni na wucin gadi gabanin a kammala ma ta mazauni na dindindin.
Shi ne ya gina makarantun sakandare na sojojin sama (Command Secondary School) guda ukku, daya a Gusau, daya a Mafara sai daya a Kaura.
Shi ne ya gina cibiyar horar da malamai ta jaha (Teachers Training And Development Centre) domin horar da malammai sanin makamar aiki.
Shi ne ya biya diyar gidaje domin ginawa tare da fadada makarantar Islamiyya ta Zawiyyar Sheikh Balarabe, Gusau a karkashin tsarin Almajiri School.
Shi ne ya biya diyar gidaje tare da fadada makarantar Islamiyya ta Malam Abdulrahaman Jelani da ke Sabon Fegi, Gusau a karkashin tsarin Almajiri School.
Shi ne ya gina makarantar Islamiyya ta Sheikh Dalla Dalla da ke Mortgage, Gusau a karkashin tsarin Almajiri School.
Shi ne ya biya diyar gidaje tare da fadada makarantar Islamiyya ta Sarkin Malamman Mafara da ke Talatar Mafara a karkashin tsarin Almajiri School.
Shi ne ya gina katafariyar makarantun furamari na zamani guda biyu, wa'yan da babu irin su a yankin jahohin arewa maso yamma, daya a bayan hukumar UBE da ke Gusau, sai kuma daya a Talata Mafara.
Shi ne ya gyara kaso mafi tsoka na makarantun furamare a jahar zamfara.
Shi ne ya gyara kaso mafi tsoka na makarantun sakandare a jahar zamfara.
Shi ne ya nemo gurabu tare da daukar nauyin wasu matasan jahar zamfara zuwa jami'o'i biyu ma su zaman kansu a jahohin Kwara da Ogun.
Wannan tamkar amsa ce zuwa ga ma su s**ar shirin Tallafin HE Yari na daukar nauyin karatun matasan jahar zamfara su 1700 ta hanyar jefa tambaya cewa mi yassa bai yi irin haka inda aka fito ba, wasu kuma su ce mi ya yi ma ilimin jahar zamfara inda aka fito.
Ba da gudunmuwa akan ilimi bai takaita kadai akan biyan WAEC da NECO ba, bai takaita akan gina sabbin makarantu da gyara wa'yan da ke akwai kadai ba, bai takaita akan gyara albashin Malammai kadai ba, bai takaita akan baiwa dalibbai tallafin karatu kadai ba, fannona ne daban daban, duk fannin da Allah ya baiwa mutum dama ba laifi ba ne ya shagaltu da shi.
Duk abun da na fada a nan bai kai kashi 1/10 na kokarin da HE Yari ya yi ma ilimi a lokacin da Allah ya ba shi damar zama gwmanan jahar zamfara ba illa na dan tsakuro ne.
Duk da irin wannan namijin kokarin da ya yi ma bangaren ilimi, amma sunan shi makiyin cigaban ilimi a wurin wasu da son zuciya ya rinjayi son gaskiyar su.
Allah ya cigaba da yi ma sa jagoranci, ya kara ba shi juriya da hankuri.
Allah dawo muna da dauwamammen zaman lafiya a jahar mu da kasar mu baki daya.
IBG
09/07/2024.