IMAMU MALIK Center JEGA

IMAMU MALIK Center JEGA Islamic Prpagation

05/04/2024

No selection process has been conducted in the kingdom and any such claims are false and misleading, the organisation The Miss Universe Organization has issued a statement denying reports that Saudi Arabia would be represented in the pageant this year. "We would like to categorically state that no...

30/03/2024

MAFI GIRMAN ABUNDA BAWA MUSULMI ZAIYI A WA'YANNAN KWANAKI(BAYAN KIYAYE FARLLAI) SHINE CIYAR DA MABUKATA

Shakka babu duk Mutumen da ya taba sauke Faralin Hajji ko Umara to ya zauna a Kasar sa ko Garin su domin taimakawa Mabukata yafi zuwansa Umara ko Hajji wanda ba na Farilla ba,
Wannan haka yake koda Kasa tana zaune Lafiya, babu Musibu irin wa'yanda Talakan Kasar nan yake fama dasu, na Tsadar Rayuwa da Lalacewar Darajar Kudaden mu,
Manzon Allah SAW, yace:
وإن أحب الأعمال إلى الله سرور تدخله على مؤمن، تكشف عنه كربا، أو تقضي عنه دينا، أو تطرد عنه جوعا)، رواه البيهقي، وحسنه الألباني.
Ma'ana:
Lallai mafi soyuwar ayuka a wurin Allah; shine farin ciki da zaka shigar a zuciyar Mumini, ko ka yaye mashi damuwa, ko ka biya mashi Bashi, kokuma ka kore mashi yunwa.
Wannan Hadisi Ingantacce da sauran Hadisai da suke dauke da ma'anasa suna nuni karara zuwaga abunda nake magana akai,

Yan Siyasar mu da masu hannu da shunin mu ku rinka tambayar Malamai kamin kuyi aiki domin sanin menene mafi dacewa mafi Falala daga cikin ayukan ku domin samun dacewa.

A irin wannan yanayi da Talakawa suke ciki a Nigeria ta Arewa Mutum ya tsaya gida ya nemi biyan Bukatunsa a wurin Allah ta hanyar Sadaka ga Mabukata zaifi saurin samun dacewa fiye da yaje Umara wadda bata Wajibi ba,
Da fatar Allah yayi Afuwa baki dayan mu.

26/03/2024

Bamu raina Malikiya ba,

Kuma bama s**ar Malikiya,

Sai dai a wurin mu Maliku ba Ma'asumi bane, domin hatta manyan Dalibansa basu daukeshi Ma'asumin ba, don haka suke saba masa,

A wurin dukkan Ahlussunnah Babu Ma'asumi sai Manzon Allah SAW!,

Don haka idan muka saba da kai a Furu'ah to ka tsaya ka natsu shin inada Magabaci akan abunda na tafi akai?, idan inada Magabaci to kada ka zargeni, kokuma ka Hantareni, yanda nayi maka Uzuri sai kayimin Uzuri nima, domin Addinin ba na gidanku bane, k**ar yanda nima ba na gidanmu bane,
Kuma shi Sabani Tilas ne a fahimta, domin Fahimta Fuska kowa da irin tashi,
Da fatar Allah ya kyauta Zukatan mu.

13/03/2024

MECECE BIDI'A A SHARI'A, KUMA SU WANENE 'YAN BIDI'A?

Tambaya:
"Ni har yanzu abun da ban gane ba shi ne WAi ita wannan bidi'ar wadda kake magana daga Ina ta fito ne?".

Amsa:

Ita wannar bidi'a da nake magana a kanta bayaninta ya fito ne daga Al- Qur'ani da Sunnar Annabi (saw).

Allah ne ya ce:
{أَمْ لَهُمْ شُرَكَاءُ شَرَعُوا لَهُمْ مِنَ الدِّينِ مَا لَمْ يَأْذَنْ بِهِ اللَّهُ } [الشورى: 21]

"Ko suna da wasu abokan tarayya wa Allah ne da s**a shar'anta musu a Addini abin da Allah bai yi izini da shi ba?".

A cikin wannar ayar sai Allah ya muzanta masu masu shar'anta wasu abubuwa a Addini wadanda Allah bai yi izini ba, su da kuma masu binsu.

Annabi (saw) ya ce:
«أما بعد، فإن خير الحديث كتاب الله، وخير الهدى هدى محمد، وشر الأمور محدثاتها، وكل بدعة ضلالة»
صحيح مسلم (2/ 592)

"Bayan haka, lallai mafi alherin magana ita ce Littafin Allah, mafi alherin shiriya shiriyar Muhammand (Manzon Allah {saw}). Mafi sharrin lamura su ne fararrunsu, kuma kowace kirkirarriyar ibada (fararriya) bata ce".

Kuma ya ce:
«من أحدث في أمرنا هذا ما ليس فيه، فهو رد»
صحيح البخاري (3/ 184)، صحيح مسلم (3/ 1343)

"Duk wanda ya farar da wani abu a cikin wannan lamari namu na Addini, abin da ba ya cikinsa to an mayar masa shi".

A wata riwayar ta Muslim:
«من عمل عملا ليس عليه أمرنا فهو رد»
صحيح مسلم (3/ 1343)

"Duk wanda ya aikata wani aiki wanda babu umurninmu a cikinsa to an mayar masa shi".

Saboda haka Addini shi ne abin da Allah ya yi izni ya shar'anta mana, Allah da Manzonsa s**a yi umurni da shi, wanda Manzonsa (saw) ya zo mana da shi a cikin Littafin Allah da Hadisansa (saw) ingantattu.
Shi ya sa duk abin da aka fare shi, wanda Allah da Manzonsa (saw) ba su yi umurni da shi ba, wanda ba ya cikin Qur'ani ko Sunna to wannan abin ba abin karba ba ne, saboda ba Addinin da Allah ya yi izni da shi ba ne, saboda bidi'a ne kirkirarriya, kuma dukkan bidi'a a Addini bata ce.

Saboda haka dukkan abin da ya saba wa Qur'ani da Sunna da Ijma'in magabata na Aqidu da Aiyuka na Ibada da Mu'amala bidi'a ne. Allah ba zai karba ba.

SU WANENE 'YAN BIDI'A?

Su ne wadanda s**a kirkiri abubuwa s**a shigar da su cikin Addini, alhali Allah bai shar'anta su ba, kuma shi da Manzonsa (saw) ba su yi umurni da su ba. Sawa'un a babin Aqida ne, ko kuma a babin Ibada ko mu'amala.

Misalan bidi'a a babin Aqida da Ibada su ne:

(1) Bidi'ar Asha'ira, sun saba wa Qur'ani da Sunna a babin Aqidun da Qur'ani da Sunna s**a zo da su, saboda suna daukan Addini ne daga hankali. Misali Allah ya fada a cikin Qur'ani cewa; yana Sama, ya daukaka a kan Al- Arshi, amma su kuma sun ce: a'a, yana ko'ina.
Allah ya ce:
{أَأَمِنْتُمْ مَنْ فِي السَّمَاءِ أَنْ يَخْسِفَ بِكُمُ الْأَرْضَ فَإِذَا هِيَ تَمُورُ (16) أَمْ أَمِنْتُمْ مَنْ فِي السَّمَاءِ أَنْ يُرْسِلَ عَلَيْكُمْ حَاصِبًا } [الملك: 16، 17]

Allah ya ce: ya daukaka a kan Al- Arshi, nan ma sun ce: a'a.
Allah ya ce:
{الرَّحْمَنُ عَلَى الْعَرْشِ اسْتَوَى } [طه: 5]

Kuma sun kore sauran siffofin Allah masu yawa, in ban da 'yan kadan da suke tabbatar da su daga 7 zuwa 20 ba. Alhali siffofin Allah suna da matukar yawa, shi ne kawai ya san yawansu.

(2) Bidi'o'in Sufaye, wadanda suke daukan Addininsu daga Mafarkai da Zauqi da sauransu.
Suna da bidi'o'i masu yawa manya da kanana, daga ciki akwai:
1- Aqidar komai Allah ne.
2- Bauta a wajen kabarbura.
3- Zikirori da Wirdi da babu su a cikin Qur'ani da Sunna.
4- Maulidi.

(3) Bidi'o'in Rafidha 'Yan Shi'a, wadanda suke daukan Addini daga karerayin da s**a jingina wa Imamansu 12 ma'asumai. Su kam bidi'o'insu sun fi na kowa yawa, har yawansu ya sa s**a banbanta da sauran Musulmai a komai. Daga ciki:
1- Aqidarsu ta Imama, wacce take hukunta inkarin Khalifancin Abubakar (ra) da Umar (ra) da Usman (ra).
2- Aqidar Isma, -wai- ma'asumai su 14 ne, Annabi (saw) da Fatima (ra) da Imamansu 12, tun daga kan Aliyu (ra) har zuwa na karshensu Mahdinsu wanda suke zaton zai zo a nan gaba. Kuma saboda wannan ne suke guluwwi a game da su, har suke ba su wasu siffofi na Allah.
3- Aqidar kafirta Sahabbai ko s**ansu da aibantasu.

(4) Bidi'ar Khawarijawa masu fita daga cikin jama'ar Musulmai, suna halatta jinanensu, suna daukan makami a kansu suna kashesu, masu guluwwi da kafirta Musulmai ba tare da hujja ba, saboda rashin ilimi da jahiltar ma'anonin Qur'ani da Sunna, wadanda Manzon Allah (saw) ya ce a kansu:
يقتلون أهل الإسلام ويدعون أهل الأوثان
صحيح البخاري (4/ 137)، صحيح مسلم (2/ 741)

"Suna kashe masu bin Muslunci, suna barin masu bautar gumaka (kafirai)".

Ibnu Umar (ra) ya ce:
«إنهم انطلقوا إلى آيات نزلت في الكفار، فجعلوها على المؤمنين»
صحيح البخاري (9/ 16)

"Sun tafi zuwa ga ayoyin da s**a sauka a kan kafirai sai s**a sanyasu a kan muminai".

A takaice magana a kan bidi'a da 'yan bidi'a tana da yawa, wannan kawai a takaice ne.

Allah ya yi mana tsari gaba daya.

Saboda haka abin da yake wajibi a kan dukkan Musulmi shi ne riko da Mazhabar Ahlus Sunna wal Jama'a, wato hanyar riko da Qur'ani da Sunna a bisa fahimtar Sahabbai da Tabi'ai da Manyan Malaman Musulunci, irin su Imamu Malik, Shafi'iy, Ahmad da sauransu. Saboda su ne suke riko da Littafin Allah da Sunnar Manzonsa (saw), kuma suke girmamasu, kuma s**a fi kowa fahimtarsu, suke binsu suke daukan Addini daga garesu, a babin Aqida da Ibada da Mu'amala da Akhlaq da sauran abubuwa na Addini, sabanin wadancan 'yan bidi'a da muka ambata, ba sa girmama Qur'ani da Sunna, ba sa daukan Addini daga garesu, kawai suna dauka ne daga son ransu da mafarke - mafarkensu da ra'ayoyin shehunnansu da shugabanninsu.

Wallahu A'alam.
Allah ya shiryar da mu gaba daya.

✍️ Dr. Aliyu Muh'd Sani
3 Mar, 2015

01/03/2024

ABBA GIDA-GIDA
Ka gaggauta yin Apology ga Malaman Kano, dakuma shi kanshi Sheikh Daurawa,
Domin Lallai kayi babban Kuskure yayinda ka Zabi yardar da Batagari akan Shara'ar Allah!,
Kuma kasani fa Sheikh Daurawa yafi Murja Kunya Tagomashi a idon Mutanen Kano, dama Nigeria baki daya,
Sannan kuma aduk Ayuka da zakayi a matsayinka na Gwamnan Kano bakada wani aiki da zaifi ayukkan Hisba Albarka, domin Hisba itace Wasika tsakanin Gwamnatoci da Mahaliccin mu.

Da fatar zaka Lura.

09/02/2024

HATTARA DAI MALAMAN AHLUSSUNNAH!,

Wannan Malamin bayada Gwani,
Don haka duk Mujamalar da Malamai zasu yimashi danganeda shiga tsakaninsa da Hukuma basu wuce ya watsa masu kasa a fuska ba,
Magana ta gaskiya kawai muyi mashi Addu'ar Allah yayi mashi Mafita kuma ya gyara mashi Usulubinsa, ya bashi Hikima tareda aiki da Basira,
Amma don Allah kada Wani Malamin Ahlussunnah ya shiga maganar sa,
Kuma Wlh Malaman mu kuyi hattara da wannan Mutumen!, baiyi k**a da mai farar Manufa ba, domin ko ba komai ai ya karanta Manhajin Salaf dangane da Mu'amala da Hukumomi dakuma Kungiyoyi amma yake saba ma Salaf da gangan, domin wata kil yanada wata Manufa,
To Wlh kuyi hattara dashi, domin duk Kasa ake Yaki da Ta'addanci to irin wannan Malamin abin gudu ne!!!.
Domin ana iya wayuwar gari fa labarinsa ya canza,sai ka jishi wani abun na daban, kuma azo ana cewa ai yana da Alaqa da wane, ai sunyi Waya da wane, ko dai da saninsa da yardarsa, kokuma Jami'an Tsaro su canza shi zuwa wani Makami na fada da Ahlussunnah, domin shima idan da ace yana da Natsuwa to da ya fahimci cewar a irin wannan Lokacin babu abunda ya k**aci Ahlussunnah a Nigeria k**ar Hadin kai tareda dunkulewa wuri daya da kuma Mutunta Juna,
Allah ya Fahimtar damu

Address

Abdussalami Street Jega
Jega
234

Telephone

+2348032092991

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when IMAMU MALIK Center JEGA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to IMAMU MALIK Center JEGA:

Share