27/03/2026
A cikin takardun da Abduljabbar ya rubutawa Attorney General na Tarayyar Nigeria, shafuka 13 ya bayyana irin yadda aka yaudare shi domin ya ci amanar kasarsa Nigeria. A faɗarsa, bai ci wannan amana ba, saboda haka aka haɗa baki da gwamnati aka saka shi cikin halin da yake ciki yanzu.
Haba Abduljabbar, ka dai yaudari kanka. Bayan an yi zama da kai karkashin kwamitin da Prof. Salisu Shehu ke jagoranta, ka fitar da audio inda ka tuba har ka janye maganganunka. Amma me ya sa daga baya ka koma kan maganganunka, bayan ka san yaudararka ake son yi domin cin amanar kasarsa Nigeria?
Wannan surutu naka cikin shafuka 13, ba abin da za su yi maka sai ƙara rikita maka case, domin an yi maka Shari’a ne kan batanci ga janibin Manzon tsira Annabi Muhammad (SAW). Ka faɗi maganganunka, an nemi ka kawo hujja cikin zama na awanni da aka yi da kai amma ka kasa.
An yi Shari’a da kai sama da shekara, duk da haka ka kasa kawo inda waɗannan mugayen maganganunka suke cikin littafan Musulunci. Yanzu kuma ga shi da bakinka kana labarta yadda aka dinga shirya cin amanar kasa da kai.
Duk ka yi shiru da bakinka a waccan lokacin saboda an yi maka alkawarin zama Khamenei a Nigeria ko Shehu Usman Danfodiyo, sai yanzu da ka ji wuya kake labartawa domin a tausaya maka?
Waɗannan maganganun na Abduljabbar s**a kara tabbatar da muhimmacin kara saka Ido sosai akan Mususs**a Dan Kala Kato.
Othman Othman