Magaji Abdullahi Idris

Magaji Abdullahi Idris Harka Islamiyya

DALILAI NA HADISI MASU NUNACEWA IYAYEN ANNABI (SAW)'YAN ALJANNA NE.Sheikh Halliru Abdullahi Maraya Kaduna.Godiya ta tabb...
01/05/2024

DALILAI NA HADISI MASU NUNA
CEWA IYAYEN ANNABI (SAW)
'YAN ALJANNA NE.
Sheikh Halliru Abdullahi Maraya Kaduna.
Godiya ta tabbata ga Allah (SWT)
da Ya ba mu dama , a jiya , muka
gabatar da wasu daga cikin dalilai
na hankali masu nuna cewa iyayen
Manzon Allah (SAW) ba 'yan wuta
ba ne . Allah (SWT) Ya kara masu
(AS)
rahama da yarda . In sha'Allah ,
yau , zamu kawo wasu dalilai na
Hadisin Manzon Allah (SAW) masu
nuna haka .
Allah (SWT) Ya kara wa ManzonSa
(SAW) matsayi da alfarma . Akwai
dalilai na Hadisin Manzon Allah
(SAW)
da suke nuna cewa iyayensa (AS)
muminai ne , 'yan
Aljanna . Daga ciki akwai :
i. Waathilah Ibnu Asqa'i (RA) ya
ce : Manzon Allah (SAW) ya ce "
Lallai Allah Ya zabi Ismaa'iil (AS)
daga cikin 'ya'yan Ibraahiim (AS) ,
kuma Ya zabi 'ya'yan Kinaanah
daga cikin 'ya'yan Ismaa'iil (AS) ,
kuma Ya zabi Quraysh daga cikin
'ya'yan Kinaanah , kuma Ya zabi
'ya'yan Haashim daga cikin
Quraysh , sannan (daga karshe)
Ya zabe ni daga cikin 'ya'yan
Haashim ."
Manazarta : Sahiihu Muslim .
ABUN DA HADISIN KE NUNAWA :
Wannan Hadisi yana nuna cewa a
cikin kowace Jama'a , tun daga
Annabi Ibraahiim (AS) har zuwa
lokacin haihuwar Manzon Allah
(SAW) , Allah (SWT) Yana zaben
mutane ne mafifita a wurinSa
(SWT) , sannan Ya sa Manzon
Allah (SAW) a tsatsonsu .
A takaice , mai lafiyayyen hankali
zai fahimta daga wannan Hadisi
cewa iyayen Manzon Allah (SAW) ,
tun daga Annabi Ibraahiim (AS)
zuwa iyayensa na haihuwa ,
zababbu ne a wurin Allah (SWT) .
Kafirai kuwa ba zababbu ba ne a
wurin Allah (SWT) . Saboda haka ,
Hadisin ya nuna cewa Abdul-Laahi
(AS) da Aaminatu (AS) , iyayen
Manzon Allah (SAW) , zababbu ne
a wurin Allah (SWT) ba 'yan wuta
ba .
ii. Sayyidunaa 'Aliyyu (RA) ya ce :
Manzon Allah (SAW) ya ce : " An
haife ni ne ta hanyar aure , ba a
fitar da ni ba ta tsatson mazinaci
tun daga Aadam (AS) har zuwa
lokacin da mahaifina da
mahaifiyata s**a haife ni ."
Manazarta : Imam At-
Tabaraaniyyu , Mu'jamul-awsad .
ABUNDA HADISIN KE NUNAWA :
Wannan Hadisi na nuna cewa
iyayen Manzo

ADDU'AR DA AKE KARANTAWA RANAR TALATA DA KUMA ZIYARATare da Dan uwan kuAminu Yahaya Muhammad (Baban Khadijah)๐Ÿ™ *ุงูŽู„ู’ุญูŽู…ู’...
16/04/2024

ADDU'AR DA AKE KARANTAWA RANAR TALATA DA KUMA ZIYARA

Tare da Dan uwan ku
Aminu Yahaya Muhammad (Baban Khadijah)๐Ÿ™

*ุงูŽู„ู’ุญูŽู…ู’ุฏู ู„ู„ู‡ูู ูˆูŽุงู„ู’ุญูŽู…ู’ุฏู ุญูŽู‚ู‘ูู‡ู ูƒูŽู…ุง ูŠูŽุณู’ุชูŽุญูู‚ู‘ูู‡ู ุญูŽู…ู’ุฏุงู‹ ูƒูŽุซูŠุฑุงู‹ ูˆูŽุงูŽุนููˆุฐู ุจูู‡ู ู…ูู†ู’ ุดูŽุฑู‘ู ู†ูŽูู’ุณู‰ ุงูู†ู‘ูŽ ุงู„ู†ู‘ูŽูู’ุณูŽ ู„ุงูŽูŽู…ู‘ุงุฑูŽุฉูŒ ุจูุงู„ุณู‘ููˆุกู ุงูู„ุงู‘ ู…ุง ุฑูŽุญูู…ูŽ ุฑูŽุจู‘ู‰ ูˆูŽุงูŽุนููˆุฐู ุจูู‡ู ู…ูู†ู’ ุดูŽุฑู‘ู ุงู„ุดู‘ูŽูŠู’ุทุงู†ู ุงู„ู‘ูŽุฐู‰ ูŠูŽุฒูŠุฏูู†ู‰ ุฐูŽู†ู’ุจุงู‹ ุงูู„ู‰ ุฐูŽู†ู’ุจู‰ ูˆูŽุงูŽุญู’ุชูŽุฑูุฒู ุจูู‡ู ู…ูู†ู’ ูƒูู„ู‘ู ุฌูŽุจู‘ุงุฑ ูุงุฌูุฑ ูˆูŽุณูู„ู’ุทุงู† ุฌุงุฆูุฑ ูˆูŽุนูŽุฏููˆู‘ ู‚ุงู‡ูุฑ ุงูŽู„ู„ู‘ู€ู‡ูู…ู‘ูŽ ุงุฌู’ุนูŽู„ู’ู†ู‰ ู…ูู†ู’ ุฌูู†ู’ุฏููƒูŽ ููŽุงูู†ู‘ูŽ ุฌูู†ู’ุฏูŽูƒูŽ ู‡ูู…ู ุงู„ู’ุบุงู„ูุจููˆู†ูŽ ูˆูŽุงุฌู’ุนูŽู„ู’ู†ู‰ ู…ูู†ู’ ุญูุฒู’ุจููƒูŽ ููŽุงูู†ู‘ูŽ ุญูุฒู’ุจูŽูƒูŽ ู‡ูู…ู ุงู„ู’ู…ููู’ู„ูุญููˆู†ูŽ ูˆูŽุงุฌู’ุนูŽู„ู’ู†ู‰ ู…ูู†ู’ ุงูŽูˆู’ู„ููŠุขุฆููƒูŽ ููŽุงูู†ู‘ูŽ ุฃูˆู„ูŠุงุกูƒ ู„ุง ุฎูŽูˆู’ููŒ ุนูŽู„ูŽูŠู’ู‡ูู…ู’ ูˆูŽู„ุง ู‡ูู…ู’ ูŠูŽุญู’ุฒูŽู†ููˆู†ูŽ*
*ุงูŽู„ู„ู‘ู€ู‡ูู…ู‘ูŽ ุงูŽุตู’ู„ูุญู’ ู„ู‰ ุฏูŠู†ู‰ ููŽุงูู†ู‘ูŽู‡ู ุนูุตู’ู…ูŽุฉู ุงูŽู…ู’ุฑู‰ ูˆูŽุงูŽุตู’ู„ูุญู’ ู„ู‰ ุงุฎูุฑูŽุชู‰ ููŽุงูู†ู‘ูŽู‡ุง ุฏุงุฑู ู…ูŽู‚ูŽุฑู‘ู‰ ูˆูŽุงูู„ูŽูŠู’ู‡ุง ู…ูู†ู’ ู…ูุฌุงูˆูŽุฑูŽุฉู ุงู„ู„ู‘ูุฆุงู…ู ู…ูŽููŽุฑู‘ู‰ ูˆูŽุงุฌู’ุนูŽู„ู ุงู„ู’ุญูŽูŠูˆุฉูŽ ุฒููŠุงุฏูŽุฉู‹ ู„ู‰ ูู‰ ูƒูู„ู‘ู ุฎูŽูŠู’ุฑ ูˆูŽุงู„ู’ูˆูŽูุงุฉูŽ ุฑุงุญูŽุฉู‹ ู„ู‰ ู…ูู†ู’ ูƒูู„ู‘ู ุดูŽุฑู‘ู ุงูŽู„ู„ู‘ู€ู‡ูู…ู‘ูŽ ุตูŽู„ู‘ู ุนูŽู„ู‰ ู…ูุญูŽู…ู‘ูŽุฏ ุฎุงุชูŽู…ู ุงู„ู†ู‘ูŽุจููŠู‘ูŠู†ูŽ ูˆูŽ ุชูŽู…ุงู…ู ุนูุฏู‘ูŽุฉู ุงู„ู’ู…ูุฑู’ุณูŽู„ูŠู†ูŽ ูˆูŽุนูŽู„ู‰ ุขู„ูู‡ู ุงู„ุทู‘ูŽูŠู‘ูุจูŠู†ูŽ ุงู„ุทู‘ุงู‡ูุฑูŠู†ูŽ ูˆูŽุงูŽุตู’ุญุงุจูู‡ู ุงู„ู’ู…ูู†ู’ุชูŽุฌูŽุจูŠู†ูŽ*
*ูˆูŽู‡ูŽุจู’ ู„ู‰ ููู‰ ุงู„ุซู‘ูู„ุงุซุงุกู ุซูŽู„ุงุซุงู‹ ู„ุง ุชูŽุฏูŽุนู’ ู„ู‰ ุฐูŽู†ู’ุจุงู‹ ุงูู„ุงู‘ ุบูŽููŽุฑู’ุชูŽู‡ู ูˆูŽู„ุง ุบูŽู…ู‘ุงู‹ ุงูู„ุงู‘ ุงูŽุฐู’ู‡ูŽุจู’ุชูŽู‡ู ูˆูŽู„ุง ุนูŽุฏููˆู‘ุงู‹ ุงูู„ุงู‘ ุฏูŽููŽุนู’ุชูŽู‡ู ุจูุจูุณู’ู…ู ุงู„ู„ู‡ู ุฎูŽูŠู’ุฑู ุงู„ุงู’ูŽุณู’ู…ุงุกู ุจูุณู’ู…ู ุงู„ู„ู‡ู ุฑูŽุจู‘ู ุงู„ุงู’ูŽุฑู’ุถู ูˆูŽุงู„ุณู‘ูŽู…ุงุกู ุงูŽุณู’ุชูŽุฏู’ููุนู ูƒูู„ู‘ูŽ ู…ูŽูƒู’ุฑูˆู‡ ุงูŽูˆู‘ูŽู„ูู‡ู ุณูŽุฎูŽุทูู‡ู ูˆูŽุงูŽุณู’ุชูŽุฌู’ู„ูุจู ูƒูู„ู‘ูŽ ู…ูŽุญู’ุจููˆุจ ุงูŽูˆู‘ูŽู„ูู‡ู ุฑูุถุงู‡ู ููŽุงุฎู’ุชูู…ู’ ู„ู‰ ู…ูู†ู’ูƒูŽ ุจูุงู„ู’ุบููู’ุฑุงู†ู ูŠุง ูˆูŽู„ููŠู‘ูŽ ุงู„ุงู’ูุญู’ุณุงู†ู .*
ูˆูŽู‡ููˆ ุจุงุณู… ุนู„ูŠู‘ ุจู† ุงู„ุญุณูŠู† ูˆู…ุญู…ู‘ุฏ ุจู† ุนู„ูŠู‘ ุงู„ุจุงู‚ุฑ ูˆุฌุนูุฑ ุจู† ู…ุญู…ู‘ุฏ ุงู„ุตู‘ุงุฏู‚ ุตู„ูˆุงุช ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ู… ุฃุฌู…ุนูŠู† ; ุฒูŠุงุฑุชู‡ู… (ุนู„ูŠู‡ู… ุงู„ุณู„ุงู…) :

*ุงูŽู„ุณู‘ูŽู„ุงู…ู ุนูŽู„ูŽูŠู’ูƒูู…ู’ ูŠุง ุฎูุฒู‘ุงู†ูŽ ุนูู„ู’ู…ู ุงู„ู„ู‡ู ุงูŽู„ุณู‘ูŽู„ุงู…ู ุนูŽู„ูŽูŠู’ูƒูู…ู’ ูŠุง ุชูŽุฑุงุฌูู…ูŽุฉูŽ ูˆูŽุญู’ูŠู ุงู„ู„ู‡ู ุงูŽู„ุณู‘ูŽู„ุงู…ู ุนูŽู„ูŽูŠู’ูƒูู…ู’ ูŠุง ุงูŽุฆูู…ู‘ูŽุฉูŽ ุงู„ู’ู‡ูุฏู‰ ุงูŽู„ุณู‘ูŽู„ุงู…ู ุนูŽู„ูŽูŠู’ูƒูู…ู’ ูŠุง ุงูŽุนู’ู„ุงู…ูŽ ุงู„ุชู‘ูู‚ู‰ ุงูŽู„ุณู‘ูŽู„ุงู…ู ุนูŽู„ูŽูŠู’ูƒูู…ู’ ูŠุง ุงูŽูˆู’ู„ุงุฏูŽ ุฑูŽุณููˆู„ู ุงู„ู„ู‡ู ุงูŽู†ูŽุง ุนุงุฑูููŒ ุจูุญูŽู‚ู‘ููƒูู…ู’ ู…ูุณู’ุชูŽุจู’ุตูุฑูŒ ุจูุดูŽุฃู’ู†ููƒูู…ู’ ู…ูุนุงุฏ ู„ุงููŽุนู’ุฏุงุฆููƒูู…ู’ ู…ููˆุงู„ ู„ุงููŽูˆู’ู„ููŠุงุฆููƒูู…ู’ ุจูุงูŽุจู‰ ุงูŽู†ู’ุชูู…ู’ ูˆูŽุงูู…ู‘ู‰ ุตูŽู„ูŽูˆุงุชู ุงู„ู„ู‡ู ุนูŽู„ูŽูŠู’ูƒูู…ู’ ุงูŽู„ู„ู‘ู‡ูู…ู‘ูŽ ุงูู†ู‘ู‰ ุงูŽุชูŽูˆุงู„ู‰ ุขุฎูุฑูŽู‡ูู…ู’ ูƒูŽู…ุง ุชูŽูˆุงู„ูŽูŠู’ุชู ุงูŽูˆู‘ูŽู„ูŽู‡ูู…ู’ ูˆูŽุงูŽุจู’ุฑูŽุฃู ู…ูู†ู’ ูƒูู„ู‘ู ูˆูŽู„ูŠุฌูŽุฉ ุฏููˆู†

31/03/2024
NAFILAR DARENA 18ANAYIN SALLAH RAKA'A 12SALLAMA 6ANAKARANTAWA AKOWACE RAKA'AFATIHA 1SABBI HISMA RABBIKA 1KULYA AYYUHAL K...
27/03/2024

NAFILAR DARENA 18

ANAYIN SALLAH RAKA'A 12
SALLAMA 6

ANAKARANTAWA AKOWACE RAKA'A

FATIHA 1
SABBI HISMA RABBIKA 1
KULYA AYYUHAL KAFIRUN 1

BAYAN ANGAMA SAI AYI WURIDIN SUNAN ALLAH

(YA NURU ) 100

DAFATAN ANSHA RUWA LFY

Usman Goga

15)ADDU'AR DA AKE KARANTAWA RANA TA 15 TA RAMADAN!ุงู„ูŠูˆู… ุงู„ุฎุงู…ุณ ุนุดุฑ : ุงูŽู„ู„ู‘ู€ู‡ูู…ู‘ูŽ ุงุฑู’ุฒูู‚ู’ู†ูŠ ููŠู‡ู ุทุงุนูŽุฉูŽ ุงู„ู’ุฎุงุดูุนูŠู†ูŽุŒ ูˆูŽุงุด...
25/03/2024

15)
ADDU'AR DA AKE KARANTAWA RANA TA 15 TA RAMADAN!
ุงู„ูŠูˆู… ุงู„ุฎุงู…ุณ ุนุดุฑ

: ุงูŽู„ู„ู‘ู€ู‡ูู…ู‘ูŽ ุงุฑู’ุฒูู‚ู’ู†ูŠ ููŠู‡ู ุทุงุนูŽุฉูŽ ุงู„ู’ุฎุงุดูุนูŠู†ูŽุŒ ูˆูŽุงุดู’ุฑูŽุญู’ ููŠู‡ู ุตูŽุฏู’ุฑูŠ ุจูุงูู†ุงุจูŽุฉู ุงู„ู’ูู…ุฎู’ุจูุชูŠู†ูŽุŒ ุจูุงูŽู…ุงู†ููƒูŽ ูŠุง ุงูŽู…ุงู†ูŽ ุงู„ู’ุฎุงุฆูููŠู†ูŽ .

Allahumma arzuqni fihi da'atal khashi'ina,
Washrah fihi sadri bi inabatil mukhbitina bi amanika ya amanal kha'ifina.

03/08/2022

TARKON ฦERA

Daga cikin raminsa, ษ—an ษ“eran na kallon sa'adda maigida ke ta cuku-cukun haษ—a masa tarko. Da ya gama sai ษ“era ya fito ya nufi wajen zakara a firgice ya ce, "abokina ka taimake ni, an sa mini tarko a gidan nan."

Zakara ya kaษ—a fiffike yai shewa ya ce, "ina ruwan maza da wankan jego? Me ya sha mini kai da tarkon da aka sa maka, ษ“arnarka ce ta jawo maka."

ฦera ya wuce wurin zomo ransa a ษ“ace ya ce, "ษ—an uwana ka taimake ni, an ษ—ana mini tarko a gidan nan."

Zomo ya harare shi ya ce, "wane ne ษ—an uwan naka? Kai dai nemi su jaษ“a da gafiya."

ฦera ya ce, "ko da ba jinsinmu ษ—aya ba, ai dukkanmu dabbobi ne, ya k**ata mu haษ—a kai mu tunkari matsalar da ta doso ษ—aya daga cikinmu."

Zomo ya ce, "wuce ka ba ni wuri! Maganinka ke nan ai, ษ“uruntunka ne ya jawo. Idan jifa ta wuce kaina, to ta faษ—a kan kowa ma."

Cikin takaici ษ“era ya nufi wajen rago ya ce masa, "ษ—an uwa ka taimake ni, an haฦ™a mini tarko."

Rago ya yi dariya ya ce, "af, to me ya haษ—a kifi da kaska kuma? Kai, ni raba ni da zancen kawai, in ka ฦ™i ko yanzu ina murje ka! Tafi ba ni wuri."

ฦŠan ษ“eran nan ya koma cikin raminsa cike da taikaicin yadda sauran dabbobi s**a baษ—a masa ฦ™asa a ido.

Can cikin dare sai aka ji kararaf! Tarko ya k**a.

ฦŠan maigidan ya zabura da sauri ya fita don ya cire gawar ษ“era daga tarkon. Ashe maciji ne ya jefa wutsiyarsa ciki. Yaro na zuwa maciji ya sare shi, aka ษ—auke shi k**ar tsumma sai asibiti. ฦŠan nan kuwa shi ke nan, ฦ™wallin ฦ™wal, ga uban.

Da safiya ta yi, maigida ya sa aka k**a zakara aka yi wa yaro dabge.

Bayan kwana biyu kuma aka yi farfesun zomo, aka kai wa yaro ya sha lagwada.

Da aka sallami yaro daga asibiti, saboda farin ciki, uban ya sa aka murฦ™ushe rago aka yanka, aka yi abinci aka raba wa maฦ™ota sadaka.

Duk wannan kicimilli da aka yi a gidan, ษ—an ษ“eran nan na cikin raminsa kwance yana kallon ikon Allah. Ya ce a ransa, 'da sun taimake ni mun kawar da tarkon, da abin da ya faru duka bai faru ba. Matsalar da ta doshi ษ—aya, za ta iya game duka.'

24/08/2021

Salam.

Yau litinin za a fara zaman juyayin Ashura a Fudiyyar garin Suleja.
09/08/2021

Yau litinin za a fara zaman juyayin Ashura a Fudiyyar garin Suleja.

Address

Minna Road
Suleja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Magaji Abdullahi Idris posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Magaji Abdullahi Idris:

Share

Category