22/07/2026
Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un.
Shahadar imam Hassan Al'mujtaba(as)!!!
Yayi Shahada ne Ranar Bakwai ga watan Safar shekara ta hamsin bayan hijira. Imam yayi shahada ne sanadiyyar Guba da matarsa (Ja'da) ta sanya masa cikin abinci.
Kadibul rawandi ya ruwaito daga imam sadiq (as) yace watarana imam Hassan (as) yana zaune da iyalinsa, sai yake cewa : Hakika ni zani mutu ne da guba kamar yadda aka kashe annabi (saw) da ita, sai s**ace wanene zai aikata maka hakan?!! sai yace masu, matata Ja'da, sai s**ace to mizai hana ka koreta daga gidan tunda ba mata daya garekaba.!! Sai imam yace " ai haryanzu bata aikata komaiba, dan haka mutane zasu iya mata uzuri s**e babu abinda tayi mani na koreta.
Ba'a dauki tsawon lokaciba mu'awuya ya aiko mata da guba akan cewa tasa masa ciki abinci, idan ta kasheshi zai aura mata dansa yazidu, kuma zai bata kudi mai yawa.
Bayan imam yayi azumi alokacin buda bakinsa, kuma ranar ana zafi mai tsanani, ta kawowa imam nono wanda tasawa guda. Bayan imam yasha sai yafara jin alamar gubar, sai yace ya aduwatallah kin kashe ni, kema Allah ya kasheki. Kuma wallahi bazaki samu abinda kikeso ba, hakika sun rudeki kuma zasu tozartaki.
Babu jimawa jikin imam yayi tsanani idan yaje zagayawa sai yan hanjinsa suke zubowa. Babu jimawa imam yayi shahada.
Dataga haka sai ta gudu gurin mu'awuya dan yabata alkawarinta sai yace lallai shi bazai aura mata dansa ba, saboda shima wani yana iya sata tabashi guba amma kudi zai bata. Bayan ta karbi kudin Allah ya jarabeta da ciwo wanda duk kudin s**a kare wajen neman magani a haka har ta mutu zuwa jahannama.
Imam (as) yayi wasiyya da a rufeshi kusa da kakansa (saw) sai Matar annabi A'isha tace lallai ita bazata yarda arufesa kusa da dakinta ba, nanndai aka samu sabani daga karshe aka tafi da gawar baki'a don arufesa, anan ma saida aka samu makiya Allah s**a jefi gawar da kibiya. Kaduba cikin littafi (مقاتل اللطالبيين)
-
Wani zai iya tanbaya miyasa imam yasan cewa ita zata bashi guba kuma yazauna da ita.
Amsa shine : Wajibi ne ga imami ma'asumi yayi mu'amala da mutane a zahirinsu, ilimin da Allah ya bashi na sani wasu abubuwa na boye, baya nufin imam yayi aiki dasu, shiyasa annabi dukda yasan munafukai acikin sahabbansa Amma bai korarsu, yana zama dasu a haka, har sai mutum yayi laifi afili kowa ya gani sai a hukuntashi. To shima imam bazai hukuntata da abinda Allah yasanar dashi ba kafin ta aikata, sai idan ta aikata.
-
Miyasa Imam hassan (as) yayi sulhu da mu'awuya.
Amsa. : Imam (as) ya shirya runduna basau dayaba wadda zai yaki mu'awuya amma mu'awuya ya sayesu da kudi yazama imam bayada mataimaka har cikin masallacin Annabi bayada aminci na rayiwarsa, saida masu binsa sallah s**a sokesa da barandami acinyarsa yayi jinya. Mafi yawan mutane basu tare dashi. Ganin haka imam (as) yayi aiki da umarnin annabi (saw) Amma abinda yayi sulhu akansa shine. Sudaina yaki - Imam (as) Shine shugaban musulmi shikuma mu'awuya zai cigaba da gudanar da siyasar musulumci abinda yashafi hudda da sauran kasashe- idan mu'awuya ya mutu, komai zai koma gurin imam. Amma duk wadannan sai da ma'awuya ya saba karshe ma yasa aka kashe imam (as).
-
اعظم الله لكم الاجر.
-
Khadim Arkam Abdulhadi (Abu Ashtar) Al'ha'riy.
Khadim Arkam A/Hadi. Abu Ashtar