Director Sabur & Co. Ltd.

Director Sabur & Co. Ltd. we sell land,industrial blocks, house for sell and rent in Abuja kano Yobe,and Borno, we have custom

Mohammed Garba
13/01/2026

Mohammed Garba

Jagoran NNPP Engr. Rabiʼu Musa Kwankwaso ya umarci duk magoya bayansa da ke riƙe da muƙamai da aka nemi su sanya hannu don su bi Gwamnati zuwa APC su sanya hannu.

Arewa Updates ta rawaito cewa, Kwankwason ya bayyana hakan ne a wani bidiyo mai tsawon mintuna 9 da sakanni 8 wanda mai taimaka masa kan yaɗa labarai Malam Saifullahi Hassan ya fitar.

Ya ce, masu riƙe da muƙamai da dama sun yi magana da shi, kuma suna cikin tashin hankali, amma ya sani lokacin rigimar da ake magana ta 2027 bai zo ba tukunna.

Kwankwaso ya ce, duk wanda aka nemi ya sa hannu don ya bi Tinubu da Ganduje ya saka hannu babu matsala.

A ƙarshe ya kuma gode wa Gwamna Abba Gida-gida kan yadda ya yabi Gwamnatinsa tare da kushe ta Ganduje a taron bada tallafi ga ɗalibai da aka yi a gidan Gwamnati.

Me za ku ce?

04/01/2026

A Maduro loyalist who is credited with stabilizing Venezuela's economy after years of crisis was picked by Trump to take over.

04/01/2026

Dalilan da su ka sanya sauya shekar Gwamna Abba zuwa APC ya samu tsaiko

An gano dalilan da s**a sa aka dage sauyin sheƙar Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, zuwa jam’iyya mai mulki ta APC, bayan an riga an kammala shirye-shirye na farko.

A ranar Juma’a, jaridar DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa gwamnan ya kammala shirye-shiryen sanar da sauyin jam’iyyarsa zuwa APC a ranar Litinin.

Kafin a dage batun sauyin jam’iyyar, hedikwatar jam’iyyar APC ta ƙasa ta shirya cewa gwamnan zai zama mutum na farko da za a yi wa rajista a Kano a sabon tsarin rajistar yanar gizo na jam’iyyar.

Bisa tsarin da aka fara tsara wa, tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje, ne zai raka gwamnan zuwa mazabarsa ta Diso domin yin rajista a shafin yanar gizon jam’iyyar tare da karɓar katin jam'iyya.

Bayan kammala rajistar gwamnan, an shirya cewa nan take zai raka Ganduje zuwa garinsa na asali a karamar hukumar Dawakin Tofa domin sabunta rajistarsa a sabon shafin yanar gizon jam’iyyar.

Sai dai wasu majiyoyi sun shaidawa DAILY NIGERIAN cewa Shugaba Bola Tinubu ne ya bayar da umarnin a dakatar da sauyin shekar ta Abba har sai an yi ƙoƙari wajen shawo kan uban gidansa na siyasa, Rabiu Kwankwaso.

A cewar majiyoyin, shirin Kwankwaso na sauya sheƙa zuwa jam’iyyar ADC ya sauya lissafin APC.

“Fadar Shugaban Ƙasa na da bayanan sirri cewa Kwankwaso ya gana da Obasanjo da Peter Obi, kuma akwai yiyuwar su haɗa kai domin kalubalantar Tinubu a 2027. Tikitin Obi/Kwankwaso haɗin gwiwa ne mai ƙarfi da zai iya sauya ma’aunin siyasar APC.

“Kuma idan babu Kwankwaso, ƙarfin siyasar gwamnan zai ragu. Saboda haka Tinubu na sake tunani kan sauyin jam’iyyar Gwamna Yusuf.

“A gaskiya ma, gwamnan ne ke neman shiga APC, ba APC ke nemansa ba. Shi ya sa har yanzu babu cikakkun sharudda kan wa zai samu wani abu a cikin rabon madafun iko bayan sauyin jam’iyyar gwamnan,” in ji wata majiya.

Sai dai wasu majiyoyi sun shaida wa wannan jarida cewa gwamnan da kansa ne ya nemi ƙarin lokaci domin ya samu damar shawo kan ƙarin mambobin Majalisar Dokoki ta Jiha da ta Ƙasa su bi sahunsa wajen sauyin jam’iyyar.

Wasu majiyoyi da ba a tabbatar da su ba sun kuma shaida wa wannan jarida cewa matsin lambar da gwamnan ke fuskanta ta sanya shi cikin ruɗani, har ta kai ga yana tunanin janye batun sauyin jam’iyyar tare da komawa ya sake haɗewa da uban gidansa Kwankwaso.

Hakazalika wasu majiyoyi na cikin gida sun tseguntawa DAILY NIGERIAN cewa an dakatar da wannan shiri ne bayan an ja hankalin gwamnan kan bukatar ya fara ganawa da manyan shugabannin APC a Kano, musamman Abdullahi Ganduje da Sanata Barau Jibrin, domin neman albarkarsu kafin ya sanar da sauyin jam’iyyar.

“Idan gwamnan ya sauya sheƙa ba tare da ya gana da Ganduje, Sanata Barau da sauran shugabannin APC ba, zai nuna kamar yana raina su. Kuma hakan ba zai yi masa kyau ba,” in ji wata majiya da ke da masaniya kan lamarin.

Ko da yake DAILY NIGERIAN HAUSA ta rawaito rahoton jaridar Platinum Post cewa gwamnan zai sanar da sauyin jam’iyyar a ranar 12 ga Janairu, wasu majiyoyi sun shaidawa DAILY NIGERIAN cewa wannan ranar ba tabbatacciya ba ce, kuma sauya shekar na iya faruwa “a kowace rana bayan ya gana da shugabannin APC na Kano.”

20/12/2025

When Herriot Tabuteau started a drug development company in 2012, he decided to do so differently. First, he’d focus on brain disorders, treatments for which are notoriously difficult to develop and whose efficacy can be hard to prove. And he’d be both CEO and the scientific founder, bringing to bear his dec­ades of experience investing in biotech startups and his medical training. But he’d take no venture capital, self-funding with help from friends and family.

Named for two parts of a nerve cell, the “axon” and the “soma,” Axsome has come a long way from its beginnings in a windowless three-desk office in New York’s Rockefeller Center, affectionately remembered as “the broom closet.”

Today, it has three drugs on the market and five in the pipeline, with the potential to help the estimated 150 million Americans suffering from conditions like depression, ADHD or Alzheimer’s disease.

Continue reading: https://www.forbes.com/sites/amyfeldman/2025/10/01/this-haiti-born-doctor-built-a-6-billion-business-developing-drugs-for-depression-and-alzheimers/?utm_campaign=ForbesMainFB&utm_source=ForbesMainFacebook&utm_medium=social
(Photo: Jamel Toppin for Forbes)

20/12/2025

For Trump, the deal delivers a titan of U.S. news and media consumption to a group of investors who have supported his political efforts.

For celebrities, businesses, and TikTok staffers that rely on the company for their livelihoods, the deal offers some certainty about the app’s future.

Investors may see limited financial benefit, but ByteDance itself — which is set to retain net roughly half of TikTok’s future U.S. profits — has much to celebrate.

Here's why Trump's TikTok deal is a win for China: https://www.forbes.com/sites/emilybaker-white/2025/12/19/why-trumps-tiktok-deal-is-a-win-for-china/?utm_campaign=ForbesMainFB&utm_source=ForbesMainFacebook&utm_medium=social (Photo: Chip Somodevilla via Getty Images)

20/12/2025

Elon Musk is entitled to his $55.8-billion Tesla pay package from 2018, Delaware's Supreme Court ruled, overturning a 2024 decision.

(Credit: AP Photo)

20/12/2025

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya buƙaci gwamnonin ƙasar su yi biyayya ga umarnin kotun ƙoli da ya bai wa ƙananan hukumomi ƴancin tafiyar da kuɗaɗensu.

Ƙarin bayani - https://bbc.in/4p3SnHe

20/12/2025

DA ƊUMI ƊUMI: Bincike ya tabbatar da cewa Addinin Musulunci Shine Addini Mafi karɓuwa a kaf faɗin duniya inda Fiye da mutane 110,000 s**a shiga Addinin Musulunci a Farkon 2025, Sannan Ya kasance a Kan Gaba Na Adadin Mutanen Da suke Shiga A shekarar 2025 - Rahoto

A yayin da shekarar 2025 ke ci gaba da tafiya, rahotanni daga sassa daban-daban na duniya na nuna ci gaba mai tarin yawa wajen yaduwar addinin Musulunci, inda dubban mutane ke karɓar Musulunci a kowace shekara.

*DUBAI (UAE):
A cikin rabin farko na shekarar 2025, Hukumar Harkokin Addini da Ayyukan Jinƙai ta Dubai (IACAD) ta bayyana cewa fiye da *mutane 3,600* ne s**a musulunta a birnin. Wannan adadi ya nuna karuwar sha’awar mutane ga addinin Musulunci, musamman ta hanyar tarbiyya da fahimtar juna tsakanin al’adu daban-daban da hukumar ke koyarwa.

*AMURKA:
A ƙasar Amurka, rahotanni sun nuna cewa fiye da *mutane 30,000* ne ke musulunta a kowace shekara. Masana sun danganta hakan da bincike da mutane ke yi kan addini, da kuma yadda Musulmi ke nuna kyawawan halaye da mu’amala a cikin al’umma.

BIRTANIYA:
A Birtaniya kuma, ana kiyasta cewa kusan *mutane 5,200* ne ke karɓar Musulunci a kowace shekara. Yawancin masu musuluntan mata ne daga cikin matasan ƙasar, musamman daga baya bayan nan

Kana Son Duba Sahihan Labarai Shigo Jaridar 👉 Wakiliya 👈 Yanzu Yi Following Karku Bari Komai Ya Wuceku...

20/12/2025
Tofa abinda wasu suke gudun yada faru Mr. Ɗangote Allah kaɗe hau
20/12/2025

Tofa abinda wasu suke gudun yada faru Mr. Ɗangote Allah kaɗe hau

'Yan kasuwa na tururuwa matatar mai ta Dangote domin saro man fetur

Matatar Dangote ta ƙarfafa matsayinta a matsayin babbar cibiyar rarraba man fetur a Nijeriya, bayan rage farashin man zuwa ₦699 kan kowace lita da kuma sauƙaƙa mafi ƙarancin adadin saye daga lita miliyan 2 zuwa lita 250,000.

Matakan sun ja hankalin ’yan kasuwar man fetur a faɗin ƙasar, inda ake samun fiye da motoci 1,000 na ɗaukar man a kullum daga matatar.

Kamfanin ya kuma ƙaddamar da tsarin garantin banki na kwanaki 10 domin tabbatar da wadatar kaya ba tare da tsaiko ba.

Shugaban Rukunin Dangote, Aliko Dangote, ya ce manufar kamfanin ita ce samar da makamashi mai rahusa kuma mai sauƙin samu ga kowane ɗan Nijeriya, yana mai jaddada cewa aikin matatar ya fi karkata ne kan bunƙasar ƙasa fiye da neman riba.

A nasu ɓangaren, Kungiyar ’Yan Kasuwar Man Fetur Masu Zaman Kansu ta Nijeriya (IPMAN) ta yi kira ga mambobinta su rika sayen man daga Matatar Dangote, tana mai tabbatar da cewa ba za a samu ƙarancin man fetur ba, duba da yadda kungiyar ke rike da sama da kashi 80 cikin 100 na kasuwar sayar da mai a ƙasar.

20/12/2025

Address

Abuja

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 09:00 - 17:00
Sunday 09:00 - 17:00

Telephone

+2348056311577

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Director Sabur & Co. Ltd. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Director Sabur & Co. Ltd.:

Share

Category