13/07/2023
YAN NIGERIANE KE NEMAN YAFIYAR KA BABA.
Irin wannan sako na da matukar taba zuciya, da bude Facebook dina yanzu "sai nake cin karo da rubutun Sayyadi Daha Azhary ya ruwauto Maulana Sheikh na cewa " Ya yafe wa dukkan Mutanen Najeriya, yanemi Kowa ya yafe masa shima, albarkan Alqur'ani Maigirma.
Sai na lura da cewa wannan zance ya fito ne a harshen karamci irin na waliyyan ALLAH, amma shi kam bai aikatawa Dan Nigeria kowanne irin laifi ba, bal dai 'Yan Nigeria su ne su kai masa laifi.
DUK WANDA YA KI SHI KO YA ZAGE SHI, BAI KISHI SABODA YA KARBE MASA WATA HAJA BA, BAI KISHI SABODA YA ZALINCESA BA, BAI KISHI SABODA YA MUNANTA MASA MU'AMALA BA, LAIFINSA SHINE "Ya Tallata masa ababen da idan ya rayu akan kiyaye lazimtarsu, to zai amfani lokacinsa, a lahira ba zai kasance cikin nadama ba, wadanda sune:
1- Istigfari.
2- Salati
3- Hailala.
SABODA HAKA, SHI SHEHU BAI DA MAKIYI A ZATIN KANSA, SAI DAI WANDA YA KIRKIRAWA KANSA KIYAYYARSA.
MU YAN NIGERIA MUNA GODIYA DA WANNAN YAFIYA DA MAULANA SHEIKH YAYI MANA, HAKIKA IDAN MUKA DUBA GIRMAN SHA'ANINSA, MUKA DUBA KARANCIN HIDIMARMU GARESHI, TO SAI MU GANE LALLAI YAYI MANA BABBAN GATA DA YA YAFE MANA.
BABA DUNIYAR MUSULUNCI BAZATA TABA MANTAWA DA KAI BA, DOMIN KAYI AIKI TUKURU WANDA YA KEREWA HIMMAR DUBBAI, ALLAH YA KARA TSAWAITA MAKA KWANA, YA KIYAYE MANA LAFIYARKA.
ALHAMDULILLAH.